Farashin Kayan Abinci Na Kara Hauhawa Ne, Inji Ministar Kudi

 


Ministar kudin Nijeriya, Hajiya Zainab Ahmad ta bayyana cewa tabbas farashin kayan abinci kara sama yake yi, ministan tayi wannan ikirarin ne bayan da   Hadimin Shugaban Kasa na musamman a bangaren watsa labarai da hulda da jama’a Garba Shehu ya yi a makon da ya gabata, inda ya bayyana cewa farashin ya fara sauka. Zainab ta bayyana haka a wani shirin safe da gidan talbijin din NTA ya yi da ita a safiyar yau Litinin.

Amma ta ce karin farashin man fetur ba zai shafi na kayan abincin ba, saboda mafiya yawan manyan motocin da suke jigilar kayan abinci a fadin kasar nan, ba da man fetur suke aiki ba, sannan ta bayyana cewa tallafin gwamnati zai yi matukar amfani a wasu fannoni ga ‘yan Nijeriya, musamman a wannan lokacin.

‘Tabbas farashin kayan abinci yana hauhawa, a kan kayan abinci yafi kamata a sanya tallafi ba a kan abubuwa irin man fetur ba, misali in ka sa mai a motarka kona shi zaka yi, ka sake sanya wa ka kona. Amma hakan ba daya bane da kayan masarufi da duk al’ummar kasa suke amfani da shi.’ Inji Zainab Ahmad