Nijeriya tana da kyakkyawar makoma Cewar Shugaban Kasa Muhammad Buhari

 

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayyana cewa yana da kwarin gwiwar cewa 'Kasar nan zata gyaru ta tsaya da kafarta fiyeda yadda take a yanzu

Buhari ya fadi  haka ne a cikin wata shimfidar Littafin Nijeriya ta cika shekaru 60 da Kamfanin  LEADERSHIP COLLECTION,  wani bangare na Rukunin  LEADERSHIP ya tattaro.
Littafin, wanda za a buga nan ba da jimawa ba, ya sanya farin ciki a cikin jama’a da kuma kamfanoni masu zaman kansu.
Wasu masu yin rijistar sun danganta kokarin a matsayin muhimmiyar alama don bikin zagayowar ranar 1 ga Oktoba da  Nijeriya ta samu ‘yancin kanta.
A cikin wani dan bangare da aka fitar a  jiya Litinin, mai taken  “Za’a Iya Yin karfi In Ana Tare”, Shugaba Buhari ya ce, “ Na yi imabi cewa, har yanzu Nijeriya tana da kyakkyawar makoma.
Inda ya kara da cewa, daga mawuyacin halin da muka shiga a baya, har yanzu akwai yiwuwar a iya  hadin kai don tabbatar da kasa daya da duk za mu yi alfahari da ita, da ban yi yakin basasa ba na kuma zama shugaban kasa na mulkin soji na dan takaitacen lokaci  na kuma yi takara har sau hudu don zama Shugaban kasa na dimokiradiyya. ”
Buhari ya bayyana kansa a matsayin “mai kyakkyawar fata, wand ya zabi ganin tafiyar Nijeriya a cikin shekaru 60 da suka gabata kamar rabin cika.”
Ya ce duk da cewa wasu na iya  yanke kauna saboda kalubalen da ke faruwa a yanzu, inda ya ce, yana da yakinin cewa, ayyukan da iyayenmu suka kafa da kuma gwarazan da suka gabata ba za su zama a banza ba. Kamar Yadda Jaridar Leadership Hausa ta rawaito