Gwamnan Ondo Akeredolu ya fita murnar lashe zaɓe.


Daga:- Aliyu Adamu Tsiga

Gwamnan jihar Ondo Rotimi Akeredolu, ya fito murna tare da magoya bayansa, jim kaɗan bayan hukumar INEC ta tabbatar masa da samun nasara.

Wannan ne karo na biyu da Mista Akeredolu ke lashe zaɓen gwamnan jihar ƙarƙashin inuwar Jam'iyyar APC.

Mista Akeredolu ya samu nasara ne kan babban abokin hamayyarsa na PDP wato Eyitayo Jegede.